Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Kotu ta dakatar da bankin CBN daga cire harajin hada-hadar kudade

Published

on

Babbar kotun tarayya dake zamanta a Awka dake jihar Anambra ta bayyana sabon tsarin babban bankin kasa CBN na hana tafiya da kudade wato (Cashless Policy) a matsayin musgunawa al’umma.

CBN dai ya aiwatar da tsarin ne a jihohi 6 tare da birnin tarayya Abuja inda abokan cinikayyar bankuna ke kokawa kan yawan cajinsu kudaden a kowace hada-hada.

Wannan ya biyo bayan karar da wani masanin shari’a a jihar ya shigar a gaban kotu ya na kalubalantar sabon tsarin na CBN yadda ya sabawa sashi na 42 a kundin tsarin mulkin kasar nan.

A na shi bangaren, Lauya mai kare babban bankin Jackson Iragunima ya ce an fito da sabon tsarin ne don saukakawa al’umma bawai don a musguna musu ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!