Connect with us

Labarai

Kwamatin amintattu na jam’iyyar adawa a Najeriya PDP ya yi watsi da rahoton kwamatin sasantawa

Published

on

Kwamatin Amintattu na jam’iyyar PDP mai adawa a Najeriya ya yi watsi da rahoton kwamatin sasantawa da aka kafa domin haɗa kan ‘ya’yan jam’iyyar a ƙasa baki ɗaya.

 

A cewar rahotonni, kwamatin ya bayar da shawara a ranar Alhamis cewa a dakatar da babban taro na Ibadan har sai an samu cikakken umarnin kotu da ya ce a yi hakan da kuma goyon hukumar zaɓe ta Inec.

 

Sannan kwamatin, ƙarƙashin jagorancin Hassan Adamu, ya bayar da shawarar kafa kwamatin riƙon ƙwarya na shugabanci saboda yawan umarnin kotuna masu karo da juna kan babban taron.

 

Sai dai wata sanarwa da shugaban kwamatin amintattun, Sanata Adolphus Wabara, ranar Juma’a ya ce shawarwarin da kwamatin sasantawar ya bayar ba su dace da matsayar shugabancin jam’iyyar ba.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!