Labarai
Kwamitin CPAC ya bukaci a gurfanar da El-Rufai a kotu ko kuma a sake shi

Kwamitin hadakar kungiyar samar da cigaban siyasa ta kasa CPAC ta bukaci gwamnatin tarayyar da ta gaggauta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a kotu ko kuma ta sake shi nan take, tana mai gargadin cewa tsare shi fiye da wa’adin da doka ta amince zai saba wa kundin tsarin mulkin kasa.
Kungiyar ta bayyana hakan ne ta bakin shugabanta ta Aminu Datti-Ahmed, inda ta ce El-Rufai ya amsa gayyatar Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati EFCC tun a ranar 16 ga watan Fabrairu.
Daga baya kuma aka mika shi ga Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC domin ci gaba da bincike kan zargin badakalar kudi.
Kungiyar ta ce umarnin tsare shi na kwanaki 14 ya riga ya kare, don haka dole ne gwamnati ta gurfanar da shi a kotu idan akwai hujja ko kuma ta sake shi, tana mai jaddada cewa Najeriya kasa ce mai bin doka kuma ba za a yi amfani da tsare mutane domin siyasa ba.
You must be logged in to post a comment Login