Connect with us

Labarai

Kwankwaso ba zai samu tikitin takara ba a 2027 – Festus Keyamo

Published

on

Ministan Harkokin Jiragen Sama da Ci gaban Sararin Samaniya, Festus Keyamo, ya bayyana cewa tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ba zai samu tikitin takarar shugaban kasa a zaben 2027 ba. Keyamo ya ce Kwankwaso ya shiga mawuyacin hali na siyasa sakamakon kin amincewa ko jinkirin karɓar tayin hadin gwiwa da jam’iyyar APC a baya.

Keyamo ya ce manyan jam’iyyun siyasa kamar APC da PDP sun karkata tikitin shugaban kasa zuwa Kudancin Najeriya a 2027, yayin da jam’iyyar NNPP da Kwankwaso ke jagoranta ke fuskantar barazanar durkushewa, musamman a Kano, sakamakon sauya sheƙar manyan ‘yan jam’iyyar zuwa APC. Ya kara da cewa ADC kuma na karkashin tasirin Atiku Abubakar ne, lamarin da ke rage wa Kwankwaso damar takara.

A cewar Keyamo, mafi kusancin damar Kwankwaso na takarar shugaban kasa ita ce a shekarar 2031, amma hakan zai dogara ne da irin shawarar siyasa da zai dauka a 2027. Ya gargadi cewa idan Kwankwaso ya rasa tasirinsa a Kano a zabe mai zuwa, hakan na iya kawo karshen burinsa na siyasa baki daya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!