Connect with us

Labarai

Kwankwaso na nan Daram a NNPP- Hashimu Dungurawa

Published

on

Shugaban jam’iyyar NNPP na jihar Kano, Hashimu Sulaiman Dungurawa, ya karyata jita-jitar da ke yawo cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen shekarar 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, zai koma jam’iyyar African Democratic Congress ADC.

 

Dungurawa, yayin da ya ke magana da manema labarai a ranar Litinin, ya bayyana cewa Kwankwaso ba ɗaya ba ne daga cikin ’yan siyasar da ke yanke shawara cikin gaggawa ba tare da zurfin tunani da la’akari da sakamakon hakan ba.

 

A cewarsa, Kwankwaso shi ne jagoran siyasa a arewacin Nijeriya, inda ya kara da cewa “kowanne dan siyasa kokari ya ke Kwankwaso ya shigo jam’iyyar su, to ta yaya za a ce wai zai  koma ADC.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!