Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Kwankwaso ya bayar da gudummuwar Asibitinsa kan Coronavirus

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabi’u Musa Kwankawaso ya bawa kwamatin yaki da cutar Corona na jihar Kano Asibitinsa na Amana a matsayin gurin da za’a rinka killace wadanda suka kamu da cutar Coronavirus.

Mataimaki na musamman ga tsohon gwamnan Rabi’u Kwankwaso kan kafafen sadarwa na zama ne Saifullahi Hassan ne ya bayyana hakan ga Freedom Radiyo ta cikin wani sakon murya daya turo mana.

Inda yace a yau Litinin Rabi’u Kwankwaso ya sanar da mallakawa gwamnatin ta Kano Asibitin nasa na Amana dake Titin Milla a unguwar Nasarawa dake nan Kano, domin yaki da wannan annoba.

Saifullahi Hassan ya kuma ce yanzu haka Asibitin na dauke da gadaje guda sittin da biyar da za’a iya kwantar da marasa lafiya akai.

Ya kuma ce ya bayar da asibitin ne biyo bayan halin da al’ummar jihar Kano suka tsinci kansu game da annobar Corona data bulla a jihar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!