Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Jami’an tsaro su kara kaimi a bakin aikin su -Baffa Babba

Published

on

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano Karota ta bukaci hukumomin tsaro da su kara kaimi a kan aikin su musamman ma a kan bakin shingayen kan hanya da a ka umarce su.

Shugaban hukumar, Dakta Baffa Babba Dan Agundi ne ya bayyana hakan  cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar Nabulisi Abubakar ya sanyawa hannu.

Ya kara da cewar gwamnatin jihar Kano ta dauki matakin ne domin ganin komai na tafiya bisa ka’ida tare da hana zirga-zirga a kan hanya wanda hakan shi ne hanyar magance yaduwar cutar a Kano.

Baffa Dan Agundi ya yi kira ga iyaye dasu kula da ‘ya’yan su saboda wasan kwallon kafa da yaran su ke gudanar da wasan a kan titina maimakon hakan su fadakar da su illar yin hakan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!