Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Laifin makara: Gwamnatin Gombe ta dakatar da ma’aikata 731

Published

on

Gwamnatin jihar Gombe ta dakatar da albashin ma’aikatan ta 731 sakamakon makarar su zuwa wajen aiki.

Wadanda aka kora an kama su da laifin makara a watan satumbar da muke ciki.

Kwamishinan kudi da tattalin arziki na jihar, Muhammad Gambo Magaji ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.

Ya ce, yanzu haka wasu mutane 170 da ake zargi da rashin zuwa aiki ana kan bincikar su.

Muhammadu Gambo Magaji, ya ce gwamnatin jihar ta samu rarar kudi da suka kai kimanin miliyon 57 da dubu dari 6 na ma’aikatan jihar da na kananan hukumomin da aka dakatar da albashin na su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!