Labarai
Gwamnatin Kano ta ladabtar da wasu jami’an lafiya bisa sakaci da aiki

Babban Daraktan Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta jihar Kano, Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim, ya ɗauki matakan ladabtarwa kan wasu ma’aikatan cibiyoyin lafiya da suka yi sakaci, tare da yabawa waɗanda suka nuna ƙwazo a bakin aiki.
Matakin ya biyo bayan ziyarar ba-zata da ya kai cibiyoyin lafiya na Tsalle da Gofaro a ƙaramar hukumar Gezawa da kuma Panshekara a Kumbotso domin duba yadda ake gudanar da ayyukan lafiya.
A cibiyoyin Tsalle da Gofaro, Daraktan ya sauke shugabannin cibiyoyin daga muƙamansu saboda rashin kulawa da yawan rashin zuwa aiki da aka samu, sannan ya ba da umarnin dakatar da albashin ma’aikatan da ba su halarci aiki ba har sai an kammala bincike.
You must be logged in to post a comment Login