Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Lauya mai kare sakataren labaran PDP ya bayyana a gaban kotu a safiyar yau

Published

on

Akalla bayan Sa’o’i 24 bayan sanar da janyewarsa daga kare tsohon Sakataren yada labaran PDP Olisa Metuh a gaban Kotu, Lauyan mai lambar kwarewa ta SAN Mista Emeka Etiaba ya sake bayyana a gaban Kotun a safiyar yau Talata.

Sai dai Olisah Metuh wanda ya yanke jiki ya fadi yayin zaman Kotun na jiya bai bayyana ba a yau, amma Emeke Etiaba ya gabatar da kansa a matsayin Lauyan Metuh.

Mai Shari’a Okon Abang ya ayyana abinda Lauyan Metun ya yi a zaman Kotun na jiya a matsayin rashin da’a da kuma kin bin ka’idojin aiki, bayan da ya fice daga cikin Shari’ar sakamakon dagewa da alkalin ya yi na ci gaba da zaman duk kuwa da faduwar Olisa Metuh.

Daga nan ne ma mai Shari’a Okon Abang y adage zaman kotun zuwa yau Talata.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!