Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ma’aikatar lafiya ta tabbatar da ɓullar Kwalara a Kano

Published

on

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta tabbatar da ɓullar cutar amai da gudawa a birnin Kano.

Babban jami’in kula da cututtuka masu yaɗuwa na ma’aikatar Sulaiman Iliyasu ne ya tabbatar da hakan a zantawarsa da Wakiliyar Freedom Radio Safara’u Tijjani Adam ta wayar tarho.

Ya ce an samu rahoton ɓullar cutar a ƙaramar hukumar Ɗanbatta wadda har aka samu asarar rayukan mutane biyu.

“A watan Afrilu mun samu rahoton ɓullar cutar amai da gudawa a Ɗanbatta wadda daga nan kuma sai cutar ta ɓulla a ƙaramar hukumar Gwarzo”.

Dr. Iliyasu ya ci gaba da cewa “Ya zuwa yanzu sama da mutane 25 zuwa 30 ne suka kamu da cutar a ƙwaryar birnin Kano kamar yadda sakamakon gwajin da muka yi ya tabbatar”.

A cewar jami’in a yanzu haka ƙananan hukumomin da suka samu ɓullar cutar sun haɗa da: karamar hukumar Dala da Ungoggo ƙaramar hukumar birni sai kuma Tarauni.

Dr. Sulaiman Isyaku ya buƙaci al’umma da su ƙara kula da tsaftar muhallansu da kuma kai rahoton duk wata cuta da ta ɓulla ga hukumomin lafiya don ɗaukan matakin gaggawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!