Connect with us

Labarai

Ma’aikatar shari’a ta Kano ta bukaci alkalai su kawo karshen cinkoso a gidaje gyaran hali

Published

on

 

 

Ma’aikatar shari’a ta Kano ta bukaci alkalai da su kawo karshen cin koson mutane da ake samu a gidajen yarin jihar ta hanyar kammala shari’un da suka dade a gaban su.

 

Hakan na cikin sanarwar da mai magana da yawun ma’aikatar Malam Najib Lawan Danbazau ya fitar.

 

A cewar sanarwar wannan na zuwa ne bayan ziyarar da sabon kwamishinan Shari’a na Kano Barrister Abdulkarim Kabiru Maude, SAN yakai kotuna da ma’aikataun shari’a dan ganin halin da suke ciki.

 

Kwamishinan ya samu rakiyar babban Sakataren ma’aikatar Barrister Salisu Muhammad Tahir da manyan daraktocinta da kuma sauran ma’aikata.

 

Haka zalika sanarwar ta ce Kwamishinan ya kai ziyara, kotunan shari’a inda ya tattauna da Grand Khadi Hon. Tijjani Ibrahim Yakasai kan dalilin da ya sa ake samun tsaikon kawo karshen wasu shari’un wanda suke daukan lokaci ba a gamasu ba, inda yace ma’aikatar shari’ar za tai aiki kafada da kafada da kotunan wajen ganin am magance cinkosan mutanan da ake samu a gidajen yarin na Kano.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!