Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Ma’aikatar wasanni ta hada gwiwa da Microsoft don horar da matasa 36,000 a Najeriya

Published

on

Ma’aikatar matasa da wasanni ta Najeriya za ta horar da matasa sama da dubu 36 ilimin fasahar zamani wato tare da hadin gwiwar kamfanin Microsoft.

Mataimakin ministan matasa da wasanni na kasa Kan harkokin yada labarai, Mista John-Joshua ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja.

Sanarwar ta kuma ce, za a gudanar da horon a cikin shekara guda mai zuwa ta 2022, karkashin sabon shirin kamfanin Microsoft mai taken: Fasahar Zamani Tare Da Sauya Mu’amala Don Cigaba.

Da yake jawabi yayin sanya hannu kan yarjejeniyar da aka kulla da Microsoft a Abuja, Ministan wasanni Sunday Dare, ya ce, ya yi farin ciki da kamfanin ya amince wajen hada gwiwa da ma’aikatar don horar da matasan Najeriya su samu ilimin fasahar zamani.

“Wannan yana da matukar mahimmanci a cikin babbar ajandar mu don daukaka samarin mu ta hanyar sama musu aikin yi ko kuma ilimin kasuwancin zamani domin dogaro da Kai,” in ji Dare.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!