Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Magudin zabe : Amurka ta sanya takunkumin hana biza ga wasu ‘yan Najeriya

Published

on

Gwamnatin Amurka ta ce ta sanya takunkumin hana biza ga wasu mutane sakamakon aikata magudi a lokacin zaben jihohin Kogi da Bayelsa a Najeriya.

Hakan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren harkokin wajen Amurka, Mike Pompeo.

Mista Pompeo, ya ce za a dauki irin wannan mataki a kan duk wanda aka samu da aikata magudi a zabukan jihohin Edo da Ondo da za a yi a watan Satumba da kuma Oktoba.

Gwamnatin Amurka ta ce duk da laifin da mutanen suka aikata, amma an nade hannu an zuba musu ido, ba tare da an dauki mataki a kan su ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!