Connect with us

Labarai

Mahmood Yakubu ya miƙa ragamar INEC ga May Agbamuche-Mbu

Published

on

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya INEC mai barin gado Farfesa Mahmood Yakubu, ya miƙa ragamar shugabancin hukumar ga Misis May Agbamuche-Mbu, wadda za ta rike matsayin shugabar hukumar ta riƙon ƙwarya.

An gudanar da bikin mika ragamar ne a ranar Talata yayin taron da yake gudana tsakanin Farfesa Yakubu da kwamishinonin zaɓe na jihohi (RECs a shalkwatar hukumar da ke Abuja.

Misis Agbamuche-Mbu, wadda ita ce tsohuwar kwamishina mafi dadewa a hukumar, za ta kula da harkokin gudanarwa na INEC har sai an naɗa sabon shugaba.

Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa ya mika shugabancin hukumar a hukumance ga Misis Agbamuche-Mbu, tare da kira ga sauran kwamishinoni da daraktoci su ci gaba da bayar da goyon baya da haɗin kai kamar yadda suka yi masa.

Wannan sauyi dai ya zo ne a dai-dai lokacin da hukumar ke ci gaba da shirye-shiryen gudanar da wasu muhimman ayyukan zaɓe a faɗin ƙasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!