Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Majalisar dinkin duniya ta dakatar da ayyukan agaji a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Rann

Published

on

Majalisar Dinkin Duniya ta dakatar da ayyukan agaji ga dubban ‘yan gudun hijirar da ke sansanin garin Rann a jihar Borno, a dalilin harin da mayakan Boko Haram suka kai kan barikin soji inda suka hallaka wasu jami’an agaji 3, wasu 3 kuma suka bace.

Sanarwar ta Majalisar dinkin duniya a Juma’ar da ta gabata, ta bayyana janye Jami ‘anta baki daya kimanin mutum 40 da ke ayyukan agaji a sansanin na Rann mai dauke da ‘yan gudun hijira akalla 55,000.

Haka zalika an dakatar da kai kayayyakin agaji zuwa sansanin na ‘yan gudun hijirar.

A daren ranar Juma’ar da ta gabata ne ita ma kungiyar Likitoci ta Najeriya Medecins sans Frontieres ta sanar da janye ayyukan ta a sansanin na Rann, sakamakon harin na mayakan Boko Haram.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!