Connect with us

Ƙetare

Majalisar dokokin Isra’ila ta kaɗa ƙuri’ar samar da ƙudirin mallake gaɓar Kogin Jordan

Published

on

Majalisar dokokin Isra’ila ta kaɗa ƙuri’a kan samar da ƙudirin mallake Gaɓar Yamma da Kogin Jordan a matsayin yankin Isra’ila.

Ƙudirin wanda wani ɗan majalisar mai tsattsauran ra’ayi ya gabatar na zuwa ne a dai-dai lokacin da Mataimakin Shugaban Amurka JD Vance ke ziyara a ƙasar domin tattauna batun tsagaita wuta a Gaza.

A watan da ya gabata, Shugaba Trump ya ce ba zai bari Isra’ila ta mamaye yankin ba, wanda Falasdinawa ke kallo a matsayin tasu kasar.

Sai dai  Jam’iyyar Firaminista Benjamin Netanyahu ba ta amince da ƙudurin dokar ba, yayin da sauran mambobin gwamnatinsa  suka amince da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!