Connect with us

Labarai

Majalisar dokokin Kano ta buƙaci gwamnati ta ɗaga darajar wasu asibitoci 4 Kumbotso

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta buƙaci gwamnatin jihar da ta ɗaga darajar wasu asibitoci guda hudu zuwa manyan Asibiti a Ƙaramar hukumar Kumbotso domin sauƙaƙawa al’ummar yankin.

 

Dan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Kumbotso Mudassir Ibrahim Zawachiki ne ya gabatar da ƙudirin gaggawa gaban majalisar a yau, cikin Asibitocin da ya buƙaci a ɗaga darajar ta su sun haɗar da na Unguwar Sheka, Na’ibawa Chiranchi sai Mariri.

 

A dai zaman majalisar na yau Ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Danbatta Murtala Musa Kore, ya gabatar da ƙudirin gaggawa kan a samarwa da al’ummar yankin Gawon bature, Dan maɗaki, Telafiya, Tukurau, Gwanda wacce zata haɗe da garin Ɓabura hanya musamman a wannan lokaci na damuna ta yadda basa iya fitowa da anfanin gona.

 

Majalisar ta tabbatar da cewa za a miƙa ƙudirin gaba domin tabbatar da an samar wa da al’ummar yankunan sauki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!