Connect with us

Labarai

Majalisar dokokin Kano ta buƙaci a ɗaga likkafar Asibitin Sakatariyar NYSC da ke Takai

Published

on

Majalisar dokokin Kano ta buƙaci gwamnatin jihar da ta ɗaga likkafar Asibitin sakatariyar NYSC da ke garin Takai zuwa babban Asibiti.

Ɗan majalisar mai wakilar Takai Musa Ali Kachako, ne ya buƙaci hakan ta cikin ƙudurin da ya gabatar a zaman majalisar na yau Litinin.

Shi ma da yake gabatar da nasa ƙudirin wakilin ƙaramar hukumar Kumbotso, Muddassir Ibrahim Zawaciki, ya gabatar da nasa ne kan neman gyaran hanyar da ta tashi daga sabon titin Madobi zuwa Riga-fada ta haɗe da garin Kumbotso.

Haka kuma a dai zaman majalisar na yau, ta yi wa ƙudurin gyaran dokar kotunan Shari’ar Muslunci da na kotunan ɗaukaka ƙara na shari’ar Muslunci karatu na biyu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!