Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin Kano ta buƙaci gwamnati ta samar da Ruwa a Dawakin Kudu

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano, ta buƙaci gwamnatin jihar Kano da ta samar da ruwan sha daga matatar ruwa ta Tamburawa ga al’ummar Mazaɓar Dawaki da Ƴan Barau da Ɗosan da yankunan Gurjiya da kuma Tsakuwa da Yankaba Tsari da mazaɓar Unguwar Duniya duk a ƙaramar hukumar Dawakin Kudu.

Majalisar ta buƙaci hakan ne bisa ƙudurin da wakilin ƙaramar hukumar Dawakin Kudu Shu’aibu Rabi’u ya gabatar a zamanta na yau Laraba.

Da ya ke gabatar da ƙudurin, ɗan majalisar ya ce, mazauna yankunan na fuskantar matsalolin rashin ruwa.

A gudunmawar da ya bayar dangane da ƙudurin, ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ƙaraye Injiniya Ahmed Ibrahim Karaye, ya bayyana Damuwa bisa yadda yankuna da dama musamman na karkara ke fama da ƙamfar ruwan amfanin yau da kullum.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!