Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar Kano ta buƙaci gwamnati ta umarci ƙananan hukumomi su riƙa raba abinci

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano, ta buƙaci gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ta umarci ƙananan hukumomin jihar nan 44 da su riƙa ware Naira miliyan 25 duk wata domin sayan kayan abinci tare da raba su ga talakawa kyauta har na tsawon wata 7.

Majalisar ta buƙaci hakan ne a zamanta na yau Laraba biyo bayan ƙudurin gaggawa da ɗan majalisar Fagge a zauren Alhaji Tukur Muhammad ya gabatar.

Yayin gabatar da ƙuɗurin, ɗan majalisar na Fagge, ya ce, a halin yanzu al’umma na majalisar cikin halin kunci ta yadda har ma wasu ke yagar Tafasa domin sarrafa ta a matsayin abinci.

Da ya ke goyon bayan ƙudurin, ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Madobi, Sulaiman Mukhtar Ishaq, ya ce, ƙudurin ya zo a lokacin da ya dace, tare da bayyana cewa ya kamata gwamnatocin ƙasar nan su gaggauta ɗaukar matakin sauƙaƙa wa al’umma wannan hali.

Ɗaukacin mambobin zauren, sun amince a kan gwamnatin ta yi amfani da hukumar CRC wajen gudanar da wannan aikin rabon kayan abinci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!