Connect with us

Labarai

Majalisar dokokin Kano ta bukaci gwamnati ta gyara masallacin Juma’a na cikin Birni

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kira ga gwamnatin Kano da ta gyara tare da sake gina masallacin Juma’a na cikin Birni, tare da gyaran hanyoyin Findi da Shangu da Kurmi a kuma Yawar a ƙaramar hukumar Rano.

Ɗan majalisar Birni Aliyu Yusuf Daneji ne ya buƙaci hakan a zaman majalisar na yau, inda ya bayyana cewa tun a baya sun miƙa kudirin ga gwamnati sai dai kawo yanzu ba a kai ga fara aikin ba.

A zaman majalisar na yau, shima ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Rano, ya yi kira ga majalisar da ta buƙaci gwamnati da ta gyara wasu daga cikin hanyoyin cikin garin Rano.

Yan majalisun biyu sun bukaci gwamnatin da ta gaggauta gyaran masallacin da kuma hanyoyin la’akari da muhimmancin su ga al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!