Labarai
Majalisar dokokin Kano ta aika wa mataimakin Gwamna takardar tuhuma

Majalisar dokokin Kano ta gayyaci mataimakin gwamna kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo da yaje ya kare kansa dangane da wasu zarge-zarge da ake masa ta hanyar aika masa takardar gayyata.
Hakan na cikin wata wasika da shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Hussaini Dala ya karanto a zauran majalisar.
Lawan Husaini Dala, shine shugaban masu rinjaye na majalisar yayi ƙarin haske kan lamarin, inda ya ce rashin bayyanar sa gaban majalisar don kare kan sa, ka iya sanya wa a tsige shi daga kan kujerar sa.
You must be logged in to post a comment Login