Connect with us

Kaduna

Majalisar kolin shari’a ta kasa reshen jihar Kaduna ta yi Allah-wadai da kalaman Rabaran Matthew Hassan Kukah

Published

on

Majalisar kolin shari’a ta kasa reshen jihar Kaduna ta yi Allah-wadai da kalaman Rabaran Matthew Hassan Kukah, wanda yace aiwatar da dokar Shari’ar Musulunci a arewacin kasar nan shi ne ya haifar da tashe-tashen hankula a yankin. Majalisar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da sakataren ta Engr. AbdurRahman Hassan ya fitar.

A cikin takardar sanarwar ya bayyana kalaman Matthew Hassan a matsayin rashin adalci, inda yace ya manta da tarihi da kuma manufar shari’ar Musulunci a yankin.

Majalisar ta kara da cewa kalaman Hassan Kukah sun nuna gazawarsa a kan fahimtar mahimmancin shari’ar Musulunci a arewacin kasar nan.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!