Labarai
Majalisar wakilai za ta yi zaman gaggawa domin duba ranakun zaben 2027

Majalisar wakilan a Najeriya za ta gudanar da zaman gaggawa a ranar Talata domin tattauna batun ranakun babban zaben shekarar 2027.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a daren a ranar Juma’a, mai magana da yawun majalisar Akin Rotimi, ya ce an sanar da mambobin majalisar zaman ne ta wata takardar cikin gida daga ofishin shugaban majalisar.
Sanarwar ta ce ‘yan majalisar za su tattauna ranakun zaben 2027 da Hukumar INEC ta sanar.
Ana sa ran zaman zai mayar da hankali kan nazarin jadawalin da INEC ta fitar da kuma yiwuwar daukar wasu matakai na doka idan bukatar hakan ta taso.
You must be logged in to post a comment Login