Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Makon muhalli: Mun Kwashe Shara Tan 4,300 a Kwanaki 13 – Dr. Kabiru Getso

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce ta kwashe shara da yawanta ya kai tan dubu 4 da ɗari 300 cikin kwanaki 13 a sassa daban daban na jihar.

Kwamishinan Muhalli Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan lokacin da ya jagorancin duba yadda aikin ya kasance.

Dakta Kabiru Getso ya ce, shirin makon muhallin na wannan shekarar da aka fara a ranar 16 ga Afirilun 2022, an kwashe sama da Tifa 787 na shara, adadin da ya kawo Tan dubu 4 da ɗari 300.

Wararen da aka kwashe tarin bila kuwa sun haɗar da: Yakasai, kofar Mata Bola “masallacin idi” a Karamar hukumar da Koki da Sarari da kuma Dandago dake Karamar hukumar Gwale dukkansu a cikin kwaryar birnin Kano.

“Shi Shirin an Samar da shi ne domin kwashe dinbin sharar da tayi yawa a cikin ƙwaryar Birnin Kano biyo bayan umarnin da gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayar na a gaggauta kwashe sharar.

“Mun shirya kammala aikin ne cikin kwanaki 10, saboda mu inganta shi sai muka ƙara kwanaki a kai kasancewar bikin ƙaramar Sallah na ƙaratowa” a cewar Getso.

Kwamishinan ya buƙaci al’umma da su guji zuba shara a magudanan ruwa, tare da Tsaftace muhallan su yadda ya kamata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!