Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu samar da dabaru a guraren zubar da shara – Dr. Kabiru Getso

Published

on

Ma’aikatar muhalli ta jihar Kano ta ce za ta samar da wasu dabaru a guraren zubar da shara a fadin jihar.

Kwamishinan Muhalli Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan, yayin taron bitar makon muhalli na shekarar 2021 da aka gudanar.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar Sunusi Kofar Na’isa ya fitar, ta ce shirin ya samu nasara matuka musamman wajen tsaftace jihar ta hanyar yashe manyan magudanan ruwa da kwashe sanannun wuraren zubar da shara.

“Mun ware mako guda don tsaftace muhalli, har ma muka kara kwanaki uku akai don bibiyar wuraren tare da tabbatar da babu wani ragowar datti a cikin al’umma” inji Kabiru Ibrahim Getso.

Dakta Getso ya kuma ce sabbin dabarun suna kan hanya musamman ma shirin gwamnati na yin yarjejeniya da wani kamfanin sarrafa shara.

“Muna da sanannun guraren zubar da shara a jihar Kano, wadanda muka yi amfani da makon muhalli wajen kwashe sharar cikin su, da suka hadar da: Kofar Wambai Kan Badala, Dorayi Gidan Sarki, Gobirawa da Naibawa ‘yan kankana, sauran su ne Rijiyar lemo ‘yan rake, Kwana shida Bonker, Yakasai ‘yan jakai da Wuju-wuju” a cewar Getso.

Dakta Kabiru Getso, ya ce, nan ba da dadewa ba jihar Kano za ta fita daga barazanar da shara ke yiwa al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!