Connect with us

Labarai

Mamallaka kafafen yaɗa labarai sun karrama Freedom Radio

Published

on

Ƙungiyar mamallaka kafafen yaɗa labarai da ke Arewacin ƙasar nan ta karrama Freedom Radio da lambar yabo, kasancewarta kafar yaɗa labarai ta farko mai zaman kanta ta ƴan Arewa.

Shugaban hukumar kula kafafen yaɗa labarai na ƙasa Alhaji Balarabe Shehu Illela ne ya miƙa lambar yabon ga shugaban tashar Freedom Radio Kano Malam Ado Sa’idu Warawa.

An dai bada lambar ne yayin taron shekara da ƙungiyar ta yi daren ranar Lahadi.

An kuma karrama muhimman mutane a Kano da sauran jihohin ƙasar nan, bisa gudunmawar da suke bai wa kafofin yaɗa labarai.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!