Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Masari ya sanya sabbin matakan gaggawa bakwai kan matsalar tsaro a Katsina

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina ta sanar da ɗaukan wasu sabbin matakai domin magance matsalar tsaro da ke addabar jihar.

A ranar Litinin ne Gwamnan jihar Alhaji Aminu Bello Masari, ya sanya hannu kan dokar sabbin matakan na gaggawa.

Mataki na farko shi ne, an rufe hanyar Jibiya zuwa Gurbin Baure, sai dai masu abin hawa su bi ta garin Funtua.

Na biyu kuma an rufe hanyar ƙanƙara zuwa Jibiya.

Na uku an hana manyan motoci ɗaukar ita ce a daji.

Mataki na huɗu an hana shigawa ko fita da dabbobi daga jihar.

Na biyar kuma shine Gwamnati ta haramta goyon mutane uku a kan Babur.

Mataki na shida kuwa shi ne, masu ƙananun motar ɗaukar fasinja kada su ɗauki sama da mutane uku.

Na bakwai shi ne, Gwamnatin ta Katsina ta hana zirga-zirga daga ƙarfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Sai mataki na bakwai ta haramta sayar da man fetur a jarka a gidajen mai.

Sai dai an yi sassaucin wannan doka a kan ƴan jarida, da jami’an tsaro da kuma ma’aikatan lafiya.

Dokar zata far aiki daga ranar Talata 31 ga watan Agustan 2021.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!