Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Abin da jama’a da masana ke cewa kan sabbin matakan da Gwamnati ta ɗauka a Zamfara

Published

on

Al’umma da masana na bayyana ra’ayoyinsu kan sabbin matakai bakwai da Gwamnatin jihar ta sanya don magance matsalar tsaro da ta addabeta.

Matakan dai sun haɗa da rufe kasuwannin jihar da hana hawa babura daga ƙarfe 6 na yamma zuwa 6 na safe da sauransu.
Me jama’a ke cewa game da hakan?

Ga ra’ayoyin waɗansu mazaunan jihar.
Bala Yaro Mada ya ce “Wannan mataki na hana sayar da mai ga jarkoki ko masu babban tanki abu ne da ya dace, kuma ya kamata duk wanda aka kama a masa hukunci”.

“Amma game da hana cin kasuwa abu ne da zai ƙara jefa talakawa cikin raɗaɗi”.

Ita kuwa wata mata da ta nemi a saka sunanta, ta ce “Gaskiya mun ji daɗi saboda matakai ne da ya kamata a ce tuntuni Gwamna ya ɗauka, fatanmu a janyo mata cikin kwamiti ɗin da aka ce an kafa, domin suma zasu bada gudunmuwa”.

Shi ma wani mazaunin Gusau cewa ya yi, “Matakin ya yi daidai domin ƴan ta’adda za su rasa samun biyan buƙatunsu, za su samu ƙarancin mai.

Dr. Sulaiman Shu’aibu Shinkafi ya ce, wannan mataki ne da ya kamata a yabawa Gwamnati kuma ya kamata kowacce jiha su ɗauki irin wannan mataki.

Ita ma wata matashiya ta ce, “Na ji daɗin waɗannan matakai, kuma ina fatan Gwamnan ya sanar da ɗaukar tsatstsauran matakai, a kan duk wanda aka samu na bai wa ƴan ta’adda bayanan sirri.

Gwamnan jihar Muhammad Bello Matawalle, ya roƙi jama’ar jihar su yi haƙuri da halin matsin da za a shiga sakamakon matakan.
Ya ci gaba da cewa, ɗaukar wannan mataki ya zama dole, domin a kare rayuwar al’ummar a jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!