Connect with us

Kaduna

Masu Bukata ta musamman zasu sami kulawa ta musamman wajen rijistan katin zabe – INEC

Published

on

Masu Bukata ta musamman zasu sami kulawa ta musamman wajen rijistan katin zabe- INEC

 

Hukumar zabe ta kasa ta ce masu bukata ta musamman, mata masu ciki da tsoffi zasu sami kulawa ta musamman idan suka je yin rijistan katin zabe.

 

Jami’ar Hulda da jama’a ta hukumar zabe, reshen jihar Kaduna Rukayyatu Sani Imam ce ta bayyana haka lokacin zantawarta Freedom Radio.

 

Rukayyatu Imam ta ce dokar hukumar zabe ta shekarar 2022 ta yi tanadin baiwa masu bukata ta musamman da mata masu ciki da tsoffi kulawa ta musamman lokacin rijistan katin zabe da kuma lokacin zabe na gama gari.

 

A cewarta, yanzu haka hukumar ta kammala rijistan mutane sama da 18, 690 a sabon rijistan da aka fara a Kaduna.

 

“Yanzu haka akwai katin zabe sama da dubu dari na shekarun baya da ba’a karba ba a Kaduna”

 

Idan za’a iya tunawa hukumar zabe ta fara rijistan katin zaben a ranar 18 ga watan Ogustan shekarar nan ta 2025.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!