Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Matsayar ECOWAS kan juyin mulkin Nijar

Published

on

Shugabannin kungiyar ECOWAS sun ba da umarnin gaggauta daukar matakin amfani da karfin soji kan gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar.

ECOWAS Sun kuma yi kira ga kungiyar Tarayyar Afirka, AU, da sauransu da su goyi bayan kudurin na kungiyar .

Kungiyar ECOWAS ta ce duk kokarin da aka yi na tattaunawa da gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar, shugabannin juyin mulkin sun yi watsi da shi, yayin da suke yin Allah wadai da ci gaba da tsare shugaba Mohamed Bazoum da iyalansa.

An cimma wannan matsaya ta shugabannin ECOWAS ne a taron koli na musamman kan harkokin siyasa a Jamhuriyar Nijar wanda ya samu halartar shugabannin kasashe takwas da ministocin harkokin wajen kasashen Laberiya da Gambia da aka kammala a Abuja.

Shugaban kasar Mauritania, Mohamed Ould Ghazouani da takwaransa na Burundi, Everiste Ndayishimiye sun halarci taron gaggawa na kungiyar ECOWAS karo na biyu kan Jamhuriyar Nijar bisa gayyatar abokan aikinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!