Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mu dage da addu’a a yayin bikin sallah – Jarman Matasan Arewa

Published

on

Sponsored 

Fitaccen ‘dan gwagwarmayar nan Ambasada Yusuf Hamza Jarman Matasan Arewa, ya nemi al’ummar musulmai musamman matasa da suyi amfani da lokacin bukukuwan sallah wajen yin addu’o’in neman zaman lafiya.

Ambasada Yusuf Hamza ya yi wannan kira ne ta cikin wata sanarwar sakon barka da sallah ga al’umma da ya fitar.

Sanarwar ta nemi al’ummar musulmai da su kaucewa amfani da wadannan lokuta wurin aikata alfasha da sunan bikin sallah.

“Mu na kira ga gwamnati da ta samar da wasu tsare-tsare da za su bunkasa rayuwar matasa, domin su ne manyan gobe” a cewarsa.

A karshe ya kara jaddada kiran al’umma kansu kara zage dantse wajen yin addu’o’I musamman a wannan wata mai albarka, domin magance matsalolin da ke addabar al’umma.

Ambassada Yusuf Hamza dai daya ne daga cikin jagororin matasan Arewa wadanda ke kan gaba wajen fafutukar inganta rayuwar matasan.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!