Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Karɓar katin zaɓe wajibi ne ga duk ɗan ƙasa nagari – Falakin Shinkafi

Published

on

Sponsored

Ambasadan zaman lafiya kuma Falakin Shinkafi Alhaji Yunusa Yusuf Hamza ya yi kira ga al’ummar Arewacin ƙasar nan da su tabbatar sun mallaki katin zaɓe domin samar da shugabanni nagari.

Falakin Shinkafi ya bayyana hakan ne, yayin zantawarsa da manema labarai.

A cewarsa katin zaɓe shi ne babban abin da talaka zai yi riƙo da shi, domin zaɓar shugabannin da zasu inganta rayuwarsa ta hanyar magance matsalolin tsaro da haɓaka tattalin arziƙi, tare da samar da abubuwan more rayuwa a birane da karkara.

”Bai kamata a ce wanda ya kai shekaru 18 a duniya ya zauna ba shi da katin zaɓe ba, duba da muhimmancin da yake da shi ga rayuwar al’umma” a cewarsa.

Ambasada Yunusa Hamza yace, karɓar katin zaɓe wajibi ne, haka shi ma yin zaɓen wajibi ne, don haka ya ƙalubalanci masu cewa ba zasu yi katin ba, saboda idan sun zaɓi shugabanni ba a ba su ko da sun lashe zaɓen.

Ya ce ”Da yin zaɓen ku bashi da amfani da Gwamnatin bata kashe maƙudan kuɗaɗe wajen shirya zaɓen ba, kuma da su kansu ƴan siyasar ba su zo wajenku nemen goyon baya ba, don haka waccan maganar bata da tushe balantana makama”.

Falakin na Shinkafi ya kuma yi kira ga shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki kan su fito da wani tsari domin wayar da kan jama’a da sake basu dama tare da sauƙaƙa musu hanyar mallakar katin zaɓen cikin sauƙi.

LABARAI MASU ALAƘA:

Barka da Sallah daga Jarman Matasan Arewa Amb. Yunusa Hamza

An naɗa Ambasada Yunusa Hamza a matsayin Falakin Shinkafi

Ambasada Yunusa Hamza:

Ɗaya ne daga cikin jagororin matasa a arewacin Najeriya wanda yayi fice wajen gina rayuwar matasa, ta hanyar koyar da su sana’o’in dogaro da kai, tare da tallafa musu wajen neman ilimi.

Yana cikin zaƙaƙuran matasan Arewa da suka yi fice wajen shigewa gaba domin kare muradan al’ummar yankin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!