Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Mun daƙile juyin mulki- Sojojin Kongo

Published

on

Dakarun sojin Jamhuriyar dimokraɗiyyar Kongo, sun bayyana cewa, sun daƙile juyin mulkin da wasu ‘yan ƙasar da na ƙetare suka kitsa wa shugaban ƙasar Felix Tshikedi a Kinshasa babban birnin ƙasar.

BBC ta ruwaito cewa, ta cikin wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin ɗin ƙasar, mai magana da yawun sojojin ƙasar Burgediya Janar Sylavin Ekenge, ya ce a yanzu ƙura ta lafa, kuma sojojin ƙasar na tsare da wasu da ake zargi da hannu a lamarin.

Haka kuma ta bayyana cewa, Jawabin nasa na zuwa ne sa’o’i bayan da wasu mutane ɗauke da makamai suka afka gidan tsohon shugaban ma’aikata kuma babban aminin shugaban ƙasar, da safiyar ranar Lahadi.

Shaidu sun ce ga wasu mutane kimanin 20 sanye da kayan sojoji sun afka wa gidan sannan suka ji ƙarar harbe-harben bindiga.

Sai dai kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ce maharan mambobin wata ƙungiya ce da ake kira ‘New Zaire Movement’ mai alaƙa da ɗan siyasar ƙasar da ke zaman gudun hijira a ƙetare, Christian Malanga.

Harin ya yi sanadiyyar mutuwar masu gadin gidan biyu da mahari guda.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!