Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun dakatar da yiwa ababen hawa rijista – Masari

Published

on

Gwamnan jihar katsina Aminu Bello Masari,ya ce umarnin dakatar da yiwa ababen hawa rajista ya biyo bayan yadda ake samun matsalar tsaro a jihar.

Hakan na cikin wata sanarwa da gwmanan jihar,Aminu Bello Masari ya fitar aka rabawa manema labarai a jihar ta katsina.

Abubuwan da gwamnatin ta hana yiwa rijistar sun hadar da motoci na gida da kuma wadanda ake haya da su.

A cewar sanarwa, dakatar da yiwa ababen hawar rajisata, wani bangare ne na kokarin kawar da ayyukan bata gari da ke addabar jihar.

Gwamnan ya kuma ce sun dakatar da safarar Dabbobi da Shanu daga jihar zuwa wasu jihohin ko shigo dasu daga wata jiha daban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!