Connect with us

Labarai

Mun kammala shirin gudanar da zaben cike gurbi na Kano- INEC

Published

on

Kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC na Kano Abdu Zango, ya tabbatar da cewa hukumar ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da zaben cike gurbi na majalisar dokokin jihar, wanda za a gudanar a ranar Asabar mai zuwa.

 

Zaben zai gudana ne a kananan hukumomin Bagwai, Shanono, tsanyawa da kuma karamar hukumar Ghari.

 

Zango Abdu ya bayyana cewa an tanadi isassun kayan aikin zabe, ma’aikata, gami da samar da tsaro, domin tabbatar da gudanar da zabe cikin gaskiya, adalci, da lumana, ba tare da tashin hankali ko tafka magudi ba.

 

Ya kuma yi kira ga ‘yan takara, jam’iyyun siyasa, da masu kada kuri’a, su gudanar da harkokinsu cikin natsuwa da mutunta dokokin zabe, tare da gujewa duk wata dabi’a da za ta iya kawo cikas ga zaman lafiya a lokacin zabe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!