Connect with us

Labarai

Mun kammala shirye-shiryen zaɓen cike gurbi na kansiloli- KANSIEC

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSIEC ta ce, ta kammala dukkan shirye-shiryen ta domin gudanar da zaɓen cike gurbi na kansiloli a mazabun Kofar Mazugal da Matan Fada da ke cikin kananan hukumomin Dala da Ghari.

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kan ta, ta kano Farfesa Sani Lawan Mulumfashi ne ya bayyana hakan a yau biyo bayan rasuwar kansilolin da ke wakiltar waɗannan mazabun biyu, inda hukumar ta bayyana cewa zaɓen zai gudana ne bisa tanadin sashi na 30 na dokar zaɓe ta shekara ta 2022.

Farfesa Sani Lawan Malumfashi ya kara da cewa zaɓen cike gurbin zai gudana a ranar 13 ga watan Disamba, shekara ta 2025, kuma sun tabbatar da shirin su na gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya da adalci.

Hukumar ta kuma mika sakon ta’aziyya ga Gwamnatin jihar Kano da kuma al’ummmar kananan hukumomin Dala da Ghari bisa wannan rashi na jagororinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!