Connect with us

Labarai

Mun kusa janye dokar dakatar da Twitter – Buhari

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce nan ba da jimawa ba za ta janye dokar dakatarwar da ta yiwa kamfanin Twitter.

Ministan yaɗa labarai da raya al’adu Alhaji Lai Muhammad ne ya bayyana hakan, yayin zantawar sa da manema labaran fadar shugaban kasa, jim kaɗan bayan kammala zaman majalisar zartarwa.

Ministan ya ce, “Matakin ƙarshe kan batun matakin dakatar da kamfanin an kusa samun matsaya”.

Alhaji Lai Muhammad ya yabawa ƴan Najeriya bisa hakurin da suka nuna, yana mai cewa, “Tuni tattaunawa ta yi nisa tsakanin gwamnatin tarayya da kamfanin kuma dab ake da cimma matsaya”.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!