Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Kamfanin Twitter ya amince da sharuddan da gwamnatin tarayya ta gindaya masa

Published

on

Kamfanin Sadarwa na Twitter ya amince da dukkan sharudan da aka gindaya masa kafin ya ci gaba da aiki a kasar nan.

Ministan yada labaran Lai Mohammed ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar Litinin.

Lai Muhammad ya ce, kamfanin Twitter na ci gaba da tattaunawa da gwamnati tare da samar da matsaya wajen ci gaba da ayyukan su a kasar nan.

A cewar Lai Muhammad, tuni shugabanin kamfanin suka amince da matakan da aka gindaya musu, tare da alkawarta mutunta ikon Najeriya, da kula da muhimman abubuwa da suka shafi tsaron kasar da hadin kai kafin dawo da shi.

Idan za a iya tunawa gwamnatin tarayya ta dakatar da amfani da shafin Twitter tun a ranar 5 ga watan Yunin 2021 sakamakon goge wani rubutu da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya wallafa a shafin sa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!