Labarai
Mun shirya domin kawar da ta’addanci Najeriya – Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa ta shirya domin ƙarfafa sojojin kasar da ke yaƙi da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a faɗin ƙasar.
Ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar kwana guda da ya kai jihar Bayelsa a ranar Juma’a, inda ya ƙaddamar da wani aiki da Gwamna Douye Diri ya yi, inda shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da baiwa dakarunta atisaye da kayan aiki domin kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro a ƙasar.
Ya jaddada cewa sun mayar da hankali wajen neman cin nasara da kawo ƙarshen duk wasu lamuran tsaro.
You must be logged in to post a comment Login