Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun shirya tsaf don kare abkuwar ambaliyar ruwa a Kano – Dr Getso

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce ta shirya tsaf don daukar matakan da suka dace na dakile faruwar ambaliyar ruwa a daminar bana.

Kwamishinan Muhalli na Jihar Kano Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan ta cikin shirin Duniyar mu Ayau na nan tashar Freedom.

Shirin Duniyar mu a yau na wannan rana ya mayar da hankali ne kan batun masu harkar ma’adanan a jihar Kanon ba bisa ka’ida ba, wanda hakan ke haifar da matsalolin muhalli ciki har da ambaliyar ruwa.

Dakta Kabiru Ibrahim Getso ya ce akwai dalilai da dama da suke haifar da ambaliyar ruwa ciki kuwa har da ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

“Akwai illa mai tarin yawa ga wadanda suke dibar ma’adanan kasa ba bisa ka’idaba,bwanda kuma hakan kan iya jefa al’ummar da ke rayuwa a yankin cikin halin damuwa, musamman zaftarewar kasa, ambaliyar ruwa da sauran matsalolin muhalli,” inji Getso.

Getso ya kuma ce kowanne albarkatun kasa na da guba mai illa musamman ga kananan yara ta fannin shafar kwakwalwar su da sauran sassan jiki.

“Rashin ilimi hakar ma’adanai shi yake janyo duk wata barazana ga muhalli wanda kuma nan ba da dadewa ba za mu kawo karshen matsalar” kamar yadda kwamishinan muhalli ya bayyana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!