Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Matawalle ya tabbatar da ‘yan bindaga sun kashe wasu mutane a Zamfara

Published

on

Gwamnan Jihar Zamfara Bello ya tabbatar da cewa ‘yan bindiga sun kashe mutane 15 sannan kuma suka sace mutane 11 a Jihar.

Bello Matawalle ya tabbatar da hakan ne a jiya yayin wani taron masu ruwa da tsaki da ya jagoranta a fadar gwamnan Jihar da ke Gusau, wanda ya hada da masu rike da sarautun gargajiya da malaman addini da kuma jami’an tsaro.

Gwamna Matawalle ya bayyana cewa ya samu rahoton yadda ‘yan bindigar suka hallaka mutane 13 tare da sace 11 a garuruwan Bingi Nahuche da ke karamar hukumar Bungudu.

Ya kara da cewa ‘Yansakai na Jihar sun yanka wasu Fulani biyu a karamar hukumar Maradun, inda ya umarci kwamishinan ‘yan sandan Jihar da ya gayyaci Sarkin Maradun Alhaji Garba Tambari da kuma Sarkin Arewan Maradun domin yin bayanin dalilin kisan fulanin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!