Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun yi haɗin gwiwa da shugabannin kasuwannin waya don gano masu yin kwace – DSP Kiyawa

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce, ta yi haɗin gwiwa da kasuwannin sayar da wayoyin hannu domin su riƙa samun bayanan masu ƙwacen waya.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala shirin “Barka da Hantsi”na nan Freedom Radio.

“Mun lura cewa kaso 70 ciki 100 na masu ƙwacen waya a jihar Kano suna ta’ammali da miyagun ƙwayoyi”.

“Wannan ne ya sanya muka ga dacewar yin haɗin gwiwa da shugabannin kasuwannin waya, domin su rikƙa ba mu rahoton wayoyin da ake kasuwancin su, kasancewar masu ƙwacen suna kai wa kasuwa domin su sayar” a cewar Kiyawa.

Kiyawa ya kuma ce, a kwanakin nan rundunar ta na samun nasarar kama masu ƙwacen waya musammana a ƙwaryar birnin Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!