Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun yi wa ma’aikatan bogi tayin afuwa -Tambuwal

Published

on

Gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya yi wa ma’aikatan bogi fiye da dubu  takwas afuwa da masu karbar albashi da ya wuce guda daya afuwa.

Hakan na kunshe cikin sanararwar da Kwamishinan kudi na jihar Alhaji Abdussamad Dasuki ya bayyana a ya yin wani taro da manema a birnin Sokoto.

Alhaji Abdulssamad Dasuki ya kara da cewar gwamnatin jihar ta dauki matakin ne don karfafawa ma’aitan da ke wannan mumunan halin da su tunawa kan su asiri, ba tare da gwamanti da kwarmata su ba ko kuma ta tuzarata su ba.

APC zata daukaka kara kan shari’ar zaben gwamnan Sokoto

SOKOTO:Asibitin koyarwa na jami’ar Usman Danfodiyo sun fara tiyatar zuciya

Gamayyar Jam’iyyun ashirin sun ki amincewa da nasarar gwamnan jihar Sokoto

Kazalika ya ce, ma’aikatan gwamnatin da suke karbar albashin da da suka bayyana wannan mumunan halin a asirice to babu shakka gwamnati zata yi musu afuwa.

A cewar Kwamishinan kudin Alhaji Abdulssamad Dasuki za a rufe karbar afuwar ne a ranar tara ga watan Disambar mai kamawa

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!