Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gamayyar Jam’iyyun ashirin sun ki amincewa da nasarar gwamnan jihar Sokoto

Published

on

Gamayyar jam’iyyun adawa guda ashirin da takwas sun ki amincewa da nasarar da gwamnan jihar Sokoto Alhaji Aminu Waziri Tambuwal ya samu na zarcewa a karo na biyu a yayin zaben gwamnan jihar da aka gudanar a baya-bayan nan.

Jam’iyyun sun bayyana matsayar ta su ce yayin wani taron manema labarai jiya a garin Sokoto.

Da ya ke jawabi a madadin sauran jam ‘iyyun, dan takarar gwamna a tutar jam’iyyar NEPP, Musa Aliyu, ya ce, gamayyar jam’iyyun baki daya ba su gamsu da sahihancin sakamakon zaben ba.

Ya ce a yayin zaben an tabka magudi da cin zarafin masu kada kuri’a wanda hakan ya sabawa dokokin zabe dama kundin tsarin mulkin kasar nan.

adi da ta gabata ne hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana Aminu Waziri Tambuwal na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya samu nasara a zaben gwamnan na jihar Sokoto.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!