Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Muna asarar tumatir a wannan lokaci – Ƴan kasuwar ƴan Kaba  

Published

on

Wani ɗan kasuwar kayan miya da ke ƴan Kaba ya kokawa kan yadda suke asarar tumatir a wannan lokaci.

Lawan Abdullahi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da Freedom Radio.

Ya ce, “Mu ƴan kasuwar kayan miya muna tafka asara a kowacce rana musamman ta tumatir, samakamon yadda yake saurin lalacewa”.

“A kowacce rana muna tafka asara ta maƙudan kuɗaɗe da mu kan mu ba mu san adadin sa ba, wannan ne ma yake mayar da kasuwancin mu baya” in ji Lawal.

Lawan Abdullahi ya kuma ce, a baya kamfanin Dangote na sayen tumatir ɗin su don sarrafawa tare da rage musu asara, sai dai a yanzu ba sa samun wannan damar.

Sai dai ya buƙaci gwamnati da ta samar musu da hanyar da za su riƙa kai tumatir ɗin nasu ana sarrafawa.

 

 

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!