Connect with us

Labarai

Muna bincike bisa kisan Ango- Yan Sandan Katsina

Published

on

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina ta ce tana bincike kan kisan wani ango da aka tsinci gawarsa cikin jini a gidansa da ke unguwar Tashar Buja a Karamar Hukumar Jibia.

wannan na cikin sanarwar da Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa an samu rahoton cewa an sami wani ango kwance cikin jini da ciwo a wuya, kuma aka garzaya da shi asibiti inda likita ya tabbatar da rasuwarsa.

Sanarwar ta ce an kama mutum guda da ake zargi da hannu a lamarin, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike domin gano hakikanin musabbabin kisan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!