Ƙetare
Mutane 66 sun mutu a harin da mayaƙan ƙungiyar ADF suka kai Demokradiyyar Congo

Aƙalla mutane 66 ne suka mutu a wani hari da mayaƙan ƙungiyar ADF mai suka kai kan jama’ar yankin Irumu na gabashin jamhuriyyar Demokradiyyar Congo mai maƙwabtaka da Uganda.
Majiyoyi sun bayyana cewa mayaƙan na ADF sun kai harin ne a Asabar ɗin ƙarshen mako kuma dukkanin mutanen da suka kashe fararen hula ne da basu ji ba basu gani ba.
Harin ya zo ne a dai dai lokacin da ake ganin lafawar tashe-tashen hankula a yankin na gabashi gab da iyakar ƙasar da Rwanda sakamakon janyewar mayaƙan M23.
Kakakin shirin Majalisar ɗinkin duniya a Congo Jean Tobie Okala, ya ce hare-haren na ADF sun ta’azzara a sassan gabashin ƙasar, inda a tsakanin ranar Alhamis zuwa Juma’ar da ta gabata mayaƙan suka kashe mutane aƙalla 30.
A wata tattaunawar sa da AP Okala ya ce bayanan da suka tattara a yankunan da ADF ta kai hare-hare ya nuna cewa an kashe fararen hular da yawansu ya kai 31 zuwa 66 a ƴan tsakanin nan.
You must be logged in to post a comment Login