Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mayaƙan ISWAP sun kashe mayaƙan Boko Haram 87

Published

on

Ƙungiyar ISWAP ta kai hari kan mayaƙan Boko Haram a wani lamari mai kama da ɗaukar fansa a yankin Tafkin Chadi.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewa mayakan boko haram 87 ne suka mutu a harin.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki biyar bayan da wasu mayaƙan Boko Haram suka kashe mayaƙan ISWAP 24 a Tsaunukan Mandara da Gaba a garin Gwoza na jihar Borno.

Mayaƙan ISWAP ɗin sun kai harin ne sansanin kwamandan Boko Haram Bakoura Modou a yankin Tafkin Chadin a ranar Laraba.

Mayaƙan ISWAP ɗin sun far wa sansanin Boko Haram ɗin ne a cikin wasu kwale-kwlae masu tsananin gudu har guda 50.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!